Min menu

Pages

News Sports

Duk Wanda Ya Kara Sa Jarumar Da Ta Fito Daga Gidan Mijinta A Fim Wuta Balbal


Furodusa kuma mai wasan barkwanci na masana’antar Kannywood, Malam Habu wanda aka fi sani da Mazaje, ya yi kira da a daina sa duk wata jarumar masana’antar da ta yi aure, sannan aurenta ya mutu ta dawo masana’antar.

A wani dan karamin bidiyo da ya fitar, Mazaje ya ce, “duk wani furodusa ya sake wata ta fito a aure ya saka ta a fim, ni babu abin da zan ce masa, sai wuta balbal.

Sannan ya rubuta a saman bidiyon cewa, “duk wata jarumar Kannywood da ta yi
aure ta fito aka sata a film, wuta balbal.”

Sai dai wani mai suna Imrana CMC ya mayar masa da martani, inda ya ce, “to kai a su wa a Kannywood? Kai da dan wasan barkwanci ne. Mazaje ba ka iya magana ba, watarana bakinka shi zai jawo a daure ka. Ka bi a hankali.”

Mazaje shi ne forodusan fim xin ‘Daga wasa’ mai dogon zango da yanzu haka ake haskawa a YouTube.

Comments

    "+html+"
"; document.querySelector("#tocDiv").innerHTML = Xhtml; document.querySelectorAll(".ScrolingToTarget").forEach(function(asd){ asd.addEventListener("click", function(e){ e.preventDefault(); document.querySelector(asd.getAttribute('href')).scrollIntoView({ behavior: 'smooth' }); });}) if (document.querySelectorAll('.amp-contnt h1,.amp-contnt h2, .amp-contnt h3, .amp-contnt h4').length == 0){ document.querySelector('ul#tocList').innerHTML = "
No titles
"; } document.querySelector('.closetoc').addEventListener('click', function(x){ document.querySelector('.topcs7v').classList.toggle('closed') }); }